Ruwan sama ya yi sanadiyyar hallaka mutane 3, da lalata Gidaje kusan 500 a kano

Date:

Daga Rahama Umar Kwaru

 

Ambaliyar ruwa ta yi ajalin mutane uku ciki har da wata yarinya ‘yar shekaru hudu tare da raunata daya da kuma raba mutane 495 da muhallansu a karamar hukumar Ajingi ta jihar Kano.

 

Sakataren zartarwa na hukumar bada agajin Gaggawa ta jihar Kano wato SEMA, Dr Saleh Jili ne ya bayyana hakan a lokacin da ya kai ziyarar jaje ga iyalan mamatan.

 

A cewarsa, sun je Ajingi ne domin jajantawa wadanda abin ya shafa, a madadin gwamnatin jihar karkashin jagorancin gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje.

Talla
Talla

 

Sakataren zartaswar SEMA, ya bayyana lamarin da ya faru bayan wanda ruwan sama kamar da bakin kwarya, yayi sanadiyar lalata gidaje dari hudu da casa’in da biyar tare da rasa rayuka uku a matsayin abin takaici.

 

Dokta Saleh Jili ya lissafa yankunan da abin ya shafa da suka hada da Toranke, Kara Malama, Chuna da Balare a karamar hukumar Ajingi.

Shin da gaske ne Kabiru Nakwango ya rasu ?

Ya ce hukumar za ta mika kayayyakin agajin ga shugaban kwamitin agajin gaggawa na karamar hukumar Ajingi, domin rabawa ga iyalan wadanda suka rasu da wadanda suka jikkata, bayan tantance wadanda abun ya shafa daga jami’an da aka dorawa alhakin lamarin.

 

Jili ya shawarci mazauna yankin da su rika share magudanun ruwa a kodayaushe, ya kuma yi kira ga mazauna kusa da kogi da tafkunan jihar nan da su tashi a halin yanzu ko kuma su kai rahoto ga ofishin SEMA domin basu tallafin da ya dace.

 

 

Tun da farko a nasa jawabin, mataimakin shugaban karamar hukumar Ajingi, Alhaji Sa’ad Ibrahim-Toranke, ya yabawa gwamnatin jihar da kuma hukumar bisa wannan agaji da aka daiwa al’ummar sa.

 

Da yake jawabi a madadin wadanda suka ci gajiyar tallafin, Malam Dayyabu Abdullahi ya yabawa hukumar da Gwamna Ganduje bisa wannan ziyarar ta’aziyya da suka kai musu.

 

“A ranar 3 ga watan Agusta an yi ruwan sama kamar da bakin kwarya wanda ya dauki sama da sa’o’i 40 wanda ya yi sanadiyyar rushewar dakuna biyu har yayi sanadiyyar hallaka‘yata ‘yar shekara 4″.inji shi

 

Kayayyakin tallafin da aka bayar sun hada da shinkafa, masara, siminti, kwanan rufi, man girki, matashin kai, wake da katifu da dai sauransu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...