Daga Rahama Umar Kwaru
Ambaliyar ruwa ta yi ajalin mutane uku ciki har da wata yarinya ‘yar shekaru hudu tare da raunata daya da kuma raba mutane 495 da muhallansu a karamar hukumar Ajingi ta jihar Kano.
Sakataren zartarwa na hukumar bada agajin Gaggawa ta jihar Kano wato SEMA, Dr Saleh Jili ne ya bayyana hakan a lokacin da ya kai ziyarar jaje ga iyalan mamatan.
A cewarsa, sun je Ajingi ne domin jajantawa wadanda abin ya shafa, a madadin gwamnatin jihar karkashin jagorancin gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje.

Sakataren zartaswar SEMA, ya bayyana lamarin da ya faru bayan wanda ruwan sama kamar da bakin kwarya, yayi sanadiyar lalata gidaje dari hudu da casa’in da biyar tare da rasa rayuka uku a matsayin abin takaici.
Dokta Saleh Jili ya lissafa yankunan da abin ya shafa da suka hada da Toranke, Kara Malama, Chuna da Balare a karamar hukumar Ajingi.
Shin da gaske ne Kabiru Nakwango ya rasu ?
Ya ce hukumar za ta mika kayayyakin agajin ga shugaban kwamitin agajin gaggawa na karamar hukumar Ajingi, domin rabawa ga iyalan wadanda suka rasu da wadanda suka jikkata, bayan tantance wadanda abun ya shafa daga jami’an da aka dorawa alhakin lamarin.
Jili ya shawarci mazauna yankin da su rika share magudanun ruwa a kodayaushe, ya kuma yi kira ga mazauna kusa da kogi da tafkunan jihar nan da su tashi a halin yanzu ko kuma su kai rahoto ga ofishin SEMA domin basu tallafin da ya dace.
Tun da farko a nasa jawabin, mataimakin shugaban karamar hukumar Ajingi, Alhaji Sa’ad Ibrahim-Toranke, ya yabawa gwamnatin jihar da kuma hukumar bisa wannan agaji da aka daiwa al’ummar sa.
Da yake jawabi a madadin wadanda suka ci gajiyar tallafin, Malam Dayyabu Abdullahi ya yabawa hukumar da Gwamna Ganduje bisa wannan ziyarar ta’aziyya da suka kai musu.
“A ranar 3 ga watan Agusta an yi ruwan sama kamar da bakin kwarya wanda ya dauki sama da sa’o’i 40 wanda ya yi sanadiyyar rushewar dakuna biyu har yayi sanadiyyar hallaka‘yata ‘yar shekara 4″.inji shi
Kayayyakin tallafin da aka bayar sun hada da shinkafa, masara, siminti, kwanan rufi, man girki, matashin kai, wake da katifu da dai sauransu.