2023: INEC ta fitar da sunan Sadiq Wali a matsayin ɗan takarar gwamna na jam’iyar PDP a Kano

Date:

Daga Zakaria Adam Jigirya

 

A ranar Juma’a ne Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta bayyana sunan Sadiq Aminu-Wali a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a jihar Kano.

 

Jam’iyyar PDP ta jihar ta rabu gida biyu, inda ko wanne bangare ya gudanar da zaben fidda gwani na jam’iyyar wanda ya haifar da Mista Wali da Muhammad Sani-Abacha dan marigayi shugaban mulkin soja a matsayin ‘yan takarar gwamna.

 

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta amince da bangaren Shehu Sagagi da ya gabatar da Mista Sani-Abacha a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar a jihar.

 

Daily Nigerian ta rawaito cewa ofishin INEC na Kano a yau Juma’a ya fitar da sunan Wali tare da abokin takararsa, Yusuf Dambatta a matsayin ‘yan takarar gwamna da mataimakinsa a zaben 2023 ba Muhammad Abacha ba.

 

Abba Kabir-Yusuf, wanda ke daga tutar jam’iyyar , NNPP, shi ma ya shiga jerin sunayen tare da abokin takararsa, Aminu Abdulsalam.

 

Haka shi ma ɗan takarar gwamna a jam’iyar PRP, Salihu Tanko Yakasai, sunansa ya fito.

 

Sannan Sheikh Ibrahim Khalil, ɗan takarar gwamna a jam’iyar ADC, yana cikin jerin sunayen.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...