Majalisar dattijai ta amince da mutanen da Buhari ke son naɗawa Ministoci

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

Majalisar dattijan Najeriya ta amince da sabbin ministoci bakwai da shugaba Muhammadu Buhari ya tura ma ta domin tabbatar da naɗinsu.

 

An tabbatar da naɗin ne bayan zaman tantace su da majalisar ta yi a zamanta na wannan Larabar.

 

Yayinda wasu daga cikin sabbin ministocin, musamman tsohon ɗan majalisa, da aka bukaci su yi gaisuwar majalisa su wuce, wasu daga cikinsu an tsare su da tambayoyi kan abubuwan da ya shafi kasa.

 

Shugaba Buhari, a wata wasika da ya aikewa majalisa mai dauke da kwanan watan 15 ga watan Yuni, 2022, ya bukaci majalisar ta amince da naɗinsa.

 

Ya ce neman bukatar amincewa da naɗin ya yi daidai da tanadin kudin tsarin mulki sashi na 147(2) na kudin tsarin mulkin shekara ta 1999 na Tarayyar Najeriya, da aka yiwa kwaskwarima.

 

Ministocin da aka tabbatar da naɗin nasu sun haɗa da: Henry Ikechukwu Ikoh – daga Abia; Umana Okon Umana – daga Akwa Ibom; Ekumankama Joseph Nkama- daga Ebonyi; da Goodluck Nanah Opiah – daga Imo.

 

Sauran su ne Umar Ibrahim El-Yakub – daga Kano; Ademola Adewole Adegoroye – daga Ondo; da Odum Udi – daga Rivers.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...