An kara samun ‘yan Najeriya miliyan 10 da suka yi rajistar zabe – INEC

Date:

Daga Auwal Alhassan Kademi

 

Sama da mutum miliyan 10 ne suka yi rajistar zabe a aikin rajistar da ake ci gaba da yi a yanzu a fadin Najeriya.

 

Hukumar zaben kasar, INEC ce ta bayyana haka a ranar Litinin.

 

Alkaluman bayanan sun nuna cewa sabbin masu rajistar sun kai 10,487,972, wadanda kuma suka kammala yin rajistar gaba daya sun kai 8,631,696.

 

Ya zuwa karfe bakwai na safiyar jiya Litinin 27 ga watan Yuni 2022, masu yin rajistar ta intanet sun kai 3,250,449, masu zuwa da kansu domin a yi musu rajistar kuwa, 5,381,247 ne.

 

BBC Hausa ta rawaito bayanin ya kuma nuna cewa daga cikin sabbin masu neman rajistar 4,292,690 maza ne yayin da 4,339,006 mata ne, masu nakasa kuma 67,171 sai matasa 6,081,456.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dan Majalisar tarayya daga Kano ya fice daga jam’iyyar NNPP

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Kano Municipal, Injiniya Sagir...

Abin mamaki: Barawo ya sace Motar dake cikin ayarin motocin gidan gwamnatin Kano

Wani barawon mota ya kutsa cikin gidan gwamnatin jihar...

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...