IPMAN ta janye batun karin farashin Man fetur a Nigeria

Date:

Kungiyar masu dillancin man fetur a Najeriya IPMAN ta janye matsayarta ta sayar da litar mai daga naira 180 zuwa sama.

 

A yanzu IPMAN ta ce za ta hakura ta ci gaba da sayar da shi a kan farashin gwamnati na naira 165.

 

A ganawa da manema labarai ranar Laraba a Abuja, Shugaban kungiyar Chinedu Okoronkwo ya ce hukumar PPMC ta amsa musu bukatun da suka gabatar.

 

A kan haka ya bukaci ‘yan Najeriya da su daina fargabar fuskantar karancin man fetur a gidajen man.

 

Mr Okoronkwo ya kara da cewa yanzu haka ana loda man daga Legas zuwa sauran yankunan kasar, kuma yana sa ran nan gaba kadan za a daina dogayen layuka a gidajen man a fadin kasar.

 

A baya IPMAN reshen jihar Legas ta bayyana cewa ba za ta iya sayar da mai kasa da naira 180 a duk lita, bayan da ta ce yanayin yadda take kashe kudi kafin sauke man a gidaje ya karu sosai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...