Sanatoci 3 sun fice daga jam’iyyar APC

Date:

Daga Aisha Aliyu Umar

Sanatoci uku na jam’iyyar APC sun yi murabus daga jam’iyyar mai mulki.

Sanatocin sun haɗa da: Ahmad Babba Kaita (Katsina ta Arewa), Lawal Gumau (Bauchi ta Kudu) da Francis Alimikhena (Edo ta Arewa).

Sanarwar murabus dinsu da sauya shekar ta su na ƙunshe ne a cikin wasiku da ko wannen ya aike wa shugaban majalisar dattawa, Ahmed Lawan ya kuma karanta yayin zaman majalisar a yau Talata.

Yayin da Kaita da Alimikhena suka sauya sheka zuwa babbar jam’iyyar adawa ta PDP, Gumau, ya koma jam’iyyar NNPP.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...