An fara samun rabuwar kawuna a APC kan wanda Buhari ke so ya gaje shi

Date:

Rahotanni na nuna alamomin soma samun rabuwar kawuna tsakanin ‘ya’yan APC kan mutumin da shugaba Buhari ke son zaɓa domin ya gaje shi a inuwar jam’iyyar.

A jiya Laraba mataimakin shugaban jam’iyyar APC reshan Arewa maso Yamma, Mallam Salihu Lukman ya aike da wata buɗaɗɗiyar wasika da ke gargaɗin cewa zaɓin Buhari na iya haifar da barazana ga jam’iyyar da shugabancinta.

Akwai kuma wasu rahotanni da ke nuna cewa ba a iya cimma matsaya a taron da gwamnonin suka yi a daren Talata kan yin sulhu a zabin marawa mutum guda, wanda shugaba Buhari ke so.

A wannan Talatar da ake saran kwamitin da ya tantace masu neman tikitin shugaban kasa a APC, ya gabatar da rahoton da ya tattara ga shugaban jam’iyya, Abdullahi Adamu.

‘Yan Najeriya dai na dako domin sannin abin da APC za ta tsayar kan ɗan takararta da kuma mutumin da zai yi gogayya da ɗan takarar da babban jam’iyyar adawa ta PDP ta tsayar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...