Gwamnatin Kano ta fayyace Gaskiyar labarin abun da ya fashe a Sabon Gari

Date:

Daga Halima Musa Abubakar
 Gwamnatin jihar Kano ta fayyace cewa abun fashewar da ya fashe a safiyar Talata a unguwar Sabon Gari makaranta ba’a Makaranta abun ya faru ba.
 Kwamishinan yada labarai na jihar Malam Muhammad Garba Cikin Wata sanarwa da ya aikowa Kadaura24, ya ce lamarin ya faru ne a wani kantin sayar da abibcin dabbobi wanda yake daura da wata makarantar da ke kan titin Aba, a unguwar Sabon Gari dake karamar hukumar Fagge.
 Ya ce duk da dai har yanzu ba’a gama tantance musabbabin fashewar abun da barnar da ya yi a hukumance ba, tuni aka fara gudanar da bincike don gano musabbabin fashewar, da asarar da ya haifar da kuma matakan da ya kamata a dauka.
 Malam Garba ya yi kira ga al’ummar jihar musamman mazauna yankin da lamarin ya faru da su kwantar da hankulansu, yayin da gwamnati tare da hadin gwiwar hukumomin da abin ya shafa ke ci gaba da gudanar da aikin.
 Kwamishinan ya tabbatar da cewa gwamnati za ta sanar da jama’a kan duk wani ci gaba da aka samu tare da gargadin mutane da su daina yada labaran da ba su da tushe balantana makama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...