Tsaka mai wuya: Shekarau ya dage taron bayyana makomarsa a yau, ko mai yasa ?

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

Sanatan kano ta tsakiya Malam Ibrahim Shekarau ya dakatar da taron da yayi niyar gudanawa a Wannan nara ta asabar.
Kadaura24 ta rawaito a dai taron na yau ne aka tsammaci Sanatan zai bayyana makomarsa a Siyasar Jihar Kano ko ya zauna a APC ko kuma ya fice daga Jam’iyyar.
Cikin wata Sanarwa da daraktan kula da Kafafen sada Zumunta na Gidan Shekarau Isama’il Lamido ya Fitar ta bayyana cewa an fasa gudanar da taron saboda wasu dalilai da bai bayyana ba.
“An dage Taron da aka shirya yi yau asabar a gidan H.E Mal Ibrahim Shekarau za a sanar da Ranar da Taron zai kasance insha Allah nan gaba kadan”. Inji Isama’il Lamido
Sai dai Sanarwa ta ce dage taron bashi da nasaba da Sulhun da jam’iyyar APC take So ayi da Sanata Shekarau.
“Akwai muhimman abubuwa da Ake karasa shirya wa tsakanin Manyan jagororin da zasu hadu Don ceto Kano Wato Madugu Uban tafiya da Malam Mai ta annabi”. Inji Lamido
Sanarwar dai ta tace anan gaba kadan za’a sanar da wata ranar yin taron.
Yanzu haka dai Rahotannin da suke zuwar mana sun tabbatar da fasa wancan taro , Inda tuni magoya bayan Sardaunan Kano suka Cika unguwar munduba Amma Kuma an hana su shiga cikin Gidan na Shekarau.
Da yawa daga cikin mahalatta wancan taro sun tsinci kawunansu cikin zullumin ko fasa taron yana da nasa ba da ziyarar da Gwamna Ganduje ya kaiwa Sardaunan a jiya Juma’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...