Tsohon Kwamishinan kasafi da Yan Majalisun Jihar Kano 3 sun fice daga APC zuwa NNPP

Date:

Wasu ‘yan majalisar dokokin jihar guda uku sun sauya sheka zuwa jam’iyyar NNPP daga APC .
 Hakan na kunshe ne a cikin wasikar sauya shekar da suka aike wa kakakin majalisar dokokin jihar Kano, inda suka sanar da majalisar sauya shekar su daga jam’iyyar APC zuwa NNPP.
A cikin sanarwar da Daraktan Yada Labarai da Hulda da Jama’a na Majalisar Dokokin Jihar Kano Uba Abdullahi ya rabawa Manema labarai, ya ce wasikun Masu dauke da kwanan watan 5/5/2022 kuma Majalisar ta karbe su a hukumance, a lokaci guda kuma Majalisar ta yi musu fatan alheri.
 A cewar sanarwar, ‘yan majalisar da suka koma jam’iyyar NNPP su ne;
 1. Hon Abdullahi Iliyasu Yaryasa Memba mai wakiltar mazabar Tudun Wada
 2. Hon.  Muhd Bello Butu,
 Memba, mai wakiltar mazabar Tofa/Rimin Gado.
 3. Hon.  Kabiru Yusuf Ismail
 Mamba, mai wakiltar mazabar Madobi
Haka zalika tsohon Kwamishinan Ma’aikatar kasafi da tsare-tsare na Jihar Kano Alhaji Nura Muhammad Dankadai shi ma ya sanar da ficewarsa daga Jam’iyyar APC zuwa Jam’iyyar NNPP.
Dankadai ya bayyana ficewar tasa ne Cikin wani sako da ya aikowa Kadaura24 a yammacin Wannan rana ta laraba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...