Gwamnan Kano 2023 : Gawuna da Garo ne yan takarar Ganduje

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida
 Rahotannin suna nuni da cewa an nada Nasir Gawuna mataimakin gwamnan Kano a matsayin wanda Zai gaji gwamna  Ganduje Kar kashin tutar jam’iyyar APC a zaben gwamna na 2023.
 An zabi Gawuna ne a wajen taron masu ruwa da tsaki da Gwamna Abdullahi Ganduje ya jagoranta, kamar yadda Jaridar Daily trust ta rawaito.
 Kadaura24 ta kuma rawaito cewa an kuma ce masu ruwa da tsakin sun amince cewa tsohon kwamishinan kananan hukumomi da masarautu, Murtala Sule Garo,  ya zama Mataimakin takarar Gawuna a zaben.
 Rahotanni sun bayyana cewa masu ruwa da tsakin sun dauko Murtala Sule Garo ne domin a sami maslaha a jam’iyyar Kuma ta kai ga gaci cikin sauki.
 Garo, wanda ake kyautata zaton shi ke da iko da tsarin jam’iyyar a matakan kananan hukumomi, ana ganin shi ne dan takarar uwargidan gwamnan, Hafsat Ganduje.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...