Iyalan Isyaka Rabi’u sun gwangwaje Sama da Limamai 100 da Suka ja Sallah da Azumi da kyautttuka

Date:

Daga Saminu Ibrahim magashi

Iyalan Marigayi sheikh Isyaka Rabi’u sun shirya walimar cin abinci tare da rabawa limaman da suka gabatar da sallar tarawi da tahajjud a masallatan khalifa shiekh ishaq rabi’u dake kwaryar birnin Kano kudade da Kuma kayan abinci.

Taron dai dama an saba gudanar da shi a duk lokaci irin wannan, wandaiyalan khalifan suke gudanarwa domin kara qarfin guiwa ga limaman da Kuma cigaba da ayyukan alkhairin da mahaifunnasu ya saba yi.

Limamai kimanin 100 ne suka rabauta da kyautar zunzurutun kudi har naira dubu ashirin da biyar biyar tare da buhunan shinkafa, inda ladanansu suka rabauta da naira dubu biyar biyar.

Walimar dai ta gudanane qarqashin jagorancin gwani Dr. yusuf ishaq rabi’u Wanda yai bayani amadadin iyalan khalifa ishaq rabi’u.

Anasu bangaren limaman sun bayyana farin cikinsu tare da addu’ar Allah ya jikan khalifa ya kuma sanya wanann kyautatawa da akaimusu a mizani.

Taron dai yasamu halarta duka iyalan khalifa dadai sauran muhimman mutane.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...

Na riga Kwankwaso shiga harkokin Siyasa – Sanata Barau Jibrin

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jaridun Amurka sun bankado Tsare-tsare uku da sojojin Amurka ke yi don tunkarar Najeriya

Rahotanni daga wasu jaridun Amurka na bayyana cewa rundunar...

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...