Daga Mubaraka Aliyu Ibrahim
Mai Neman jam’iyyar APC ta tsayar da shi takarar Shugaban kasa a zabe Mai zuwa Asiwaju Bola Ahmad Tinubu ya rabawa Kungiyoyin a Kano buhunhunan shinkafa domin tallafa musu a Wannan lokaci na Ramadan.
Tsohon Kwamishinan matasa da wasanni na jihar kano Alhaji Kabiru Ado lakwaya, Wanda shi ne Shugaban Kwamitin rabon Kayan sh ne ya bayyana hakan yayin Kaddamar da rabon Kayan a Gidan Gwamnatin Jihar Kano.
Tsohon Kwamishinan yace Bola Tinubun ya raba Kayan ne domin tallafawa al’ummar Jihar kano a kokarin da yake na saukakawa Rayuwar al’umma Musamman a wannan lokaci na Ramadan.
Yace za a raba kayan ne ga kungiyoyi daban-daban dake jihar Nan,Inda aka raba musu kanana da Manyan buhunhunan shinkafa har Dubu daya da dari takwas.
Wasu daga cikin Waɗanda Suka amfana da tallafin sun godewa Bola Ahmad Tinubu bisa Wannan tallafi da ya baiwa Rukunonin Kungiyoyi daban-daban dake jihar kano.