Saudiyya ta baiwa Nigeria adadin Mutane dubu 43 da zasu sauke farali a bana – Muhd Abba Danbatta

Date:

Daga Aisha Gwadabe

Mahukunta a Kasar Saudiyya sun bayyana cewa sun baiwa Nigeria adadin mutune dubu 43 ne za su sauke farali a bana.

Babban sakataren hukumar Jin dadin alhazai na Kano Muhammad Abba Danbatta ne ya sanar da hakan yayin taron manema Labarai a ranar Laraba.

Muhd Danbatta ya ce hakan ya biyo bayan yadda kasar Saudiyya ta ce adadin mutune Milyan daya ne kadai za su gudanar da aikin hajjin bana a fadin duniya.

Ya ce wannan adadi da aka baiwa Najeria na da alaka da yawan mutanen da Najeria ta ke da shi.

Muhammad Danbatta ya ce ko da yake har yanzu Hukumar kula da aikin hajji ta Kasa NAHCON bata fitar da kudin aikin hajjin bana ba Amma alamu na nuna kudin zai karu fiye da yadda aka biya a shekarun baya

Ya ce a baya an canja Dala akan 350 yanzu kuma ta Kai 408 da ke nuna lallai za a samu Karin kudin.

A yanzu dai ana jiran hukumar kula da Aikin hajji ta Kasa NAHCON ta baiwa kowacce jiha adadin kujerunta tare da bayyana adadin kudin Aikin hajjin na bana.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...