Ku daina haihuwar ‘ya’yan da kuka san ba ku da halin kula da su – in ji Nafisa Abdullahi

Date:

Daga Sadeeq  Sa’eed Sulaiman

Fitacciyar tauraruwar fina-finan Kannywood, Nafisa Abdullahi, ta yi kira ga masu haihuwar ‘ya’ya ba tare da kula da su ba da su guji yin haka.

Ta bayyana haka ne a wasu sakonni da ta wallafa a shafinta na Tuwita ranar Asabar.

“Ku daina haihuwar ‘ya’yan da kuka san ba ku da halin kula da su,” in ji Nafisa.

Ta kara da cewa Allah zai tuhumi mutanen da suke haifar ‘ya’ya ba tare da sauke nauyin da ya dora musu ba.

A cewarta: “Kun ga dukkan mutanen da ke haifar ‘ya’yan da ba su ji ba ba su gani ba, domin kawai su aika da su almajiranci, kuma su ci gaba da haifar karin ‘ya’ya, Allah sai ya saka wa yaran nan!!!”

Ta bayyana matukar bacin ranta kan yadda wasu iyaye suke tura ‘ya’yansu ‘yan shekara biyu zuwa uku almajirci.

Tauraruwar ba ta ambaci sunayen wadanda take yi wa wannan gargadi ba, sai dai dama ba sabon abu ba ne yadda a kasar Hausa ake tura kananan yara almajirci.

Wannan lamari ya dade yana bata wa mutane da dama rai, musamman ganin cewa wasu na zargi ana amfani da irin wadannan yara wajen aikata laifuka.

Sai dai kalaman tauraruwar sun jawo martani daban-daban inda wasu suke yaba mata yayin da wasu suke sukar ta.

Da yake tsokaci, M.M Dambatta, ya jinjina wa tauraruwar sannan ya ce “har yanzu na kasa fahimtar yadda uba zai aika dansa dan shekara biyar domin ya kula da kansa da sunan almajirci. Ya kamata a tsayar da wannan lamari.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...

Na riga Kwankwaso shiga harkokin Siyasa – Sanata Barau Jibrin

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jaridun Amurka sun bankado Tsare-tsare uku da sojojin Amurka ke yi don tunkarar Najeriya

Rahotanni daga wasu jaridun Amurka na bayyana cewa rundunar...

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...