Kano Pillars za ta dawo buga wasa a Kano

Date:

 

Hukumar kula da gasar firimiya ta Najeriya, Nigeria Professional Football League (NPFL), ta bai wa ƙungiyar ƙwallon kafa ta Kano Pillars damar ci gaba da buga wasanni a filin wasanta na Sani Abacha da ke Kano.

Wata sanarwa da hukumar ta aike wa kulob ɗin ta ce an ba shi damar ce bayan duba na tsanaki.

Hukumar ta ce wajibi ne Kano Pillars ta tanadi wani filin wasan da za ta ci gaba da buga wasanni da zarar an fara aikin gyara ciyawar filin taka leda ta filin kafin kammala shi.

Pillars ta ce ta amince da sharaɗin, har ma ta ce za ta buga wasanta na gaba tare da Katsina United a gida Kano ranar 16 ga watan Afrilu.

Pillars ba ta buga wasa a gida ba a kakar bana sakamakon matakin da NPFL ta ɗauka, inda ta umarci a sauya ciyawar filin taka ledar.

Yanzu haka Pillars na mataki na 13 da maki 26 bayan buga wasa 22 a kakar bana ta 2022/23.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...

Na riga Kwankwaso shiga harkokin Siyasa – Sanata Barau Jibrin

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jaridun Amurka sun bankado Tsare-tsare uku da sojojin Amurka ke yi don tunkarar Najeriya

Rahotanni daga wasu jaridun Amurka na bayyana cewa rundunar...

Dalibai 22 sun kammala karatu da daraja ta 1 a bikin yaye ɗalibai na farko na Jami’ar Baba-Ahmed Kano

Jami’ar Baba-Ahmed, Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai...