Idan gwamnatin tarayya ta gaza, za mu ɗauki sojojin haya don kare al’ummarmu – El-Rufai

Date:

 

Gwamnan Jihar Kaduna  Nasir El-Rufai ya yi barazanar cewa shi da sauran gwamnonin yankin za su ɗauki sojojin haya don kare rayukan mutanensu idan gwamnatin tarayya ƙarƙashin Shugaba Buhari ta kasa kawo ƙarshen hare-haren ‘yan fashi a yankin.

Da yake magana da manema labarai jim kaɗan bayan ya gana da Buharin a ranar Juma’a, El-Rufai ya ce ba ‘yan fashin daji ne suka kai hari kan jirgin ƙasa na Kaduna zuwa Abuja ba – “yan Boko Haram ne”.

“Na faɗa wa shugaban ƙasa cewa wallahi idan ba a ɗauki mataki ba wannan abin ba zai tafi ba…dole sai dai mu gwamnoni mu ɗauki mataki don kare rayukan al’ummarmu,” in ji shi.

“Ko da hakan na nufin ɗaukar sojojin haya don su zo su yi aikin, za mu yi hakan don kawo ƙarshen lamarin.”

Sai dai gwamnan ya ce shugaban ƙasa ya faɗa masa cewa gwamnati za ta ɗauki matakin daƙile hare-haren a watanni masu zuwa.

Wasu rahotanni sun sha zargin cewa gwamnatin Najeriya ƙarƙashin tsohon Shugaba Goodluck Jonathan ta ɗauki sojojin haya don yaƙar Boko Haram a arewa maso gabas, amma babu tabbas game da rahoton saboda gwamnatin ba ta taɓa bayyana haka ba.

Harin da ‘yan bindigar suka kai kan jirgin ƙasa a yammacin Litinin da ta gabata ya yi sanadiyyar mutuwar mutum aƙalla takwas tare da raunata kusan 40. Har yanzu ba a tantance yawan waɗanda suka yi garkuwa da su ba

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...