An dakatar da Limamin Apo saboda sukar Buhari kan harin bam na jirgin kasa a Kaduna

Date:

Daga Mubaraka Aliyu Abubakar
 Kwamitin gudanarwa na masallacin ya dakatar da babban limamin masallacin Juma’a na Apo da ke Abuja, Sheikh Nuru Khalid, saboda sukar da ya yi wa shugaban kasa Muhammadu Buhari kan harin bam na jirgin kasa na Kaduna.
 Kadaura24 ta rawaito Limamin, a cikin hudubarsa ta Juma’a, ya soki shugaban kasa kan gazawar sa ta zuwa Kaduna don ganin Waɗanda harin ta’addancin da aka kai ya rutsa da su.
 Ya ce shugaban ya je Kaduna domin yakin neman zabe, amma ya ki zuwa jihar bayan harin bam don ya jajantawa al’umma.
 “Shugaban kasa Buhari yace wai yana Allah wadai, Kowa ma ai yayi Allah wadai da faruwar lamarin, in banda ‘yan ta’adda, ya kamata shugaban kasa ya ziyarci jihar domin jajantawa wadanda abin ya shafa”. Inji Malamin
 Shugaban kwamitin kula da masallacin, Sai’du Dansadau, ya ce an dakatar da malamin ne saboda hudubar da yayi a ranar 1 ga Afrilu ta za iya tunzura al’umma.
 Ya bayyana cewa Shehun Malamin ya yi wa’azi na hana al’umma yin abun da kundin tsarin mulkin Kasa ya basa, ta hanyar shawartar masu zabe da su baiwa siyasa sharadi kafin zaben su.
  Dansadau ya kara da cewa wa’azin ya sabawa tsarin addinin Musulunci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...