Daga Sayyadi Abubakar Gwagwarwa
Dan kishin kasar nan Falakin Shinkafi Amb. Yunusa Yusuf Hamza ya bayyana tsaftar Muhalli da cewa hanyace ta inganta Lafiyar al’umma da Kuma gojewa dumamar yanayi.
Kadaura24 ta rawaito Falakin Shinkafin ya bayyana hakan ne lokacin da yake ganawa da wakilin Kadaura24 a unguwar Yakasai dake Karamar Hukumar birni a jihar kano.
Yace tsaftar Muhalli wajibi ce ga al’umma, matukar suna buƙatar gujewa yaduwar cututtuka Waɗanda suke hallakawa ko jikkata al’umma, Inda ya ce rashin tsaftar Muhalli Kan jawo cututtuka a cikin al’umma Waɗanda ake rasa musabbabin yaduwar su.
” Idan al’umma Suna tsaftace Muhalli su za a Sami sauki wajen yakar cututtuka da matsalar dumamar yanayi da a yanzu haka ake fama da ita ko’ina a duniya”. Inji Amb. Yunusa Yusuf
Yace ” Idan har kasashen da suka cigaba, a kullum zasu Rika Neman Hanyar da zasu yaki dumamar yanayi, to Babu shakka mu kuwa kamata yayi mu tunkari matsalar tun daga tushe, tunda dai bamu kai su ba karfin tattalin arziki ba”. Inji Falakin Shinkafi
Amb. Yunusa Yusuf Hamza ya ce ya shiga an yi aikin tsafar muhalli na Karshen wata ne domin nuna muhimmancin hakan ga sauran al’umma Musamman Matasa da Sauran al’umma.
Yayi fatan masu ruwa da tsaki a Cikin al’umma zasu rika shiga harkokin cigaban al’ummar su domin yin hakan zai baiwa yan baya damar yin koyi da abubuwan alkhairi da suka ga manyansu Suna yi.

