Sarkin Kanurin a kano ya yabawa Malamai bisa addu’o’in Zaman Lafiya da suke yi

Date:

Daga Rabi’u Usman

Sarkin Kabilar Kanuri mazauna jihar kano Alhaji Mustapha Lawan, kuma Wakilin Shehun Borno a jihar Kano ya kai ziyarar neman Goyon bayan Malamai a nan kano musamman wajen rawar da suke takawa wajen taimakawa da Addu’oin neman zaman lafiya a jihar Kano dama kasa baki daya.

Sarkin Kanurin ya kai ziyara ne ga Babban Limamin masallacin Murtala Sheikh Malam Badamasi Dan Taura, inda ya nemi Limamin daya karfafawa Jama’a gwiwa wajen yin Addu’a ga shugabanni da kuma zaman lafiya, tare da kwanciyar hankali harma da hada kan kabilar kanuri a nan kano domin zama tare a matsayin kasa daya Al’umma daya.

Yana mai cewar, akwai kyakkyawan Alaka tsakanin malaman jihar kano da kasar Borno kamar yadda tarihi ya nuna tun a baya, musamman ta fannin cinikayya da mutanen Borno ke shigowa kano, yayin da su kuma mutanen kano suke zuwa borno neman ilimi.

A nasa bangaren Babban Limamin Masallacin Murtala Malam Badamasi Dan Taura ya Jaddada Goyon Bayan sa ga sarkin da kuma tabbatar dayin Addu’a ga jihar kano dama kasa baki daya.

Yana mai cewar, ta haka ne za’a samar da shugabanni na gari da zasu jagoranci Al’ummar jihohi dama kasa baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...