Gwamnatin mu za ta zama kamar gada tsakanin mulkin dattawa da matasa – Atiku Abubakar

Date:

Alhaji Atiku Abubakar, tsohon mataimakin shugaban Najeriya, ya ƙaddamar da takarar neman shugabancin ƙasar a babban zaɓe na 2023 mai zuwa a jam’iyyar adawa ta PDP.

Atiku, wanda ya shafe shekara fiye da 15 da suka wuce yana neman shugabancin Najeriya, ya ce zai mayar da hankali kan ɓangare uku idan aka zaɓe shi a matsayin shugaban ƙasa.

Da ya ke jawabi yayin taron, Atiku ya ce gwamnatinsa za ta zama gada tsakanin mulkin dattijai da na matasa.

“Gwamnatinmu za ta zama kamar gada ce [da za ta haɗa] tsakanin mulkin dattijai da na matasa.”

Ya ci gaba da cewa: “A ƙarƙashin mulkina, zan mayar da hankali kan ɓangare biyar masu muhimmanci; haɗin kan Najeriya, tsaro, tattalin arziki, ilimi, ciyar da ɓangarorin gwamnatin tarayya gaba da ƙara musu iko.”

Bikin ya gudana a International Conference Centre da ke Abuja a yau Laraba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...