Yan sanda a Kano sun fara farautar makusancin Shekarau, Bashir Gentile

Date:

Daga Sayyadi Abubakar Sadeeq
 Rundunar ‘yan sanda a Kano na shirin cafke wani shahararren mai sharhi kuma mai sharhi kan al’amuran siyasa, Bashir Gentile, kan sukar gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje, a wasu shirye-shiryen rediyo na cikin gida, kamar yadda Jaridar DAILY NIGERIAN ta rawaito.
 Bashir Gentile, wanda na hannun dama ne ga tsohon gwamnan jihar, Ibrahim Shekarau, kuma mai taimaka wa shugaban majalisar dattawa Ahmad Lawan a halin yanzu.
 A baya-bayan nan dai da dama daga cikin masu sukar gwamnan suna fuskantar tuhuma a gaban Alkalai bayan ‘yan sanda sun kama su.
Rahotanni sun nuna cewa bayan yunkurin kama Bashir Gentile ya ci tura, a yanzu ‘yan sanda sun gayyace shi domin ya amsa tambayoyi kan karar da aka shigar a kansa.
 Da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Abdullahi Kiyawa, ya ce bai da masaniya akan gayyata ko shirin kama Bashir Gentilen.
 SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce zai kara yin bincike kan lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...