Wata Gidauniya ta bada kyautar Littattafai sama da dubu ga makarantun firamare a K/H Garun Mallam

Date:

Daga Safyanu Dantala Jobawa
  Wata Ƙungiya mai suna Naziru educational foundation ta bada kyautar littattafan Karatu ga makarantun firamare don inganta sha’anin ilmi yaran yankin.
Da yake gabatar da Littattafan a gaban iyayan daliban, Shugaban Gidauniyar Comrade Naziru Dan-Hajiya Yadakwari, ya ce wannan taimakon na ɗaya daga cikin irin gudunmuwar da za su rinka bayarwa don kara inganta harkokin rayuwar al’umma ta fannoni daban-daban a karamar hukumar Garun mallam.
 Ya bayyana Gidauniyar da  cewar, za ta cigaba da tallafawa Mata da Ƙananan Yara da Marasa Ƙarfi domin taimaka masu.
 “Ilimi na daya daga cikin wani ɓangaren da muka baiwa fifiko, shi yasa muka bayar da Littattafan rubutu fiye da dubu domin inganta sha’anin koyo da koyarwa a makarantunmu don inganta rayuwar’ya’yan mu”. Com. Naziru
 A nasa jawabin tsohon shugaban karamar humar Garun mallam kuma babban bako a wajen, Alh, Abdu Sule Yadakwari, ya yi bayani mai tsaho Kan muhimmancin Ilimi da kuma yadda ya kamata al’umma su rika Shiga harkokin Ilimi ta fuskar ba da tallafi a harkar.
Daga nan ya buƙaci masu hannu-da-shuni a yankin da su rinka taimaka wa a ɓangaren ilmi, domin shi kaɗai ne makamin da za’a iya magance matsalolin tsaro da shan miyagun ƙwayoyi a tsakanin al’umma.
Wakilin Kadaura24 ya ruwaito mana cewar iyayen yaran, sun gode wa shugaban wannan gidauniya ta Naziru educational foundation a bisa namijin kokarin da ya nuna a karamar hukumar Garun mallam duba da irin halin da sha’anin ilimi ke ciki a wannan karnin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Abin mamaki: Barawo ya sace Motar dake cikin ayarin motocin gidan gwamnatin Kano

Wani barawon mota ya kutsa cikin gidan gwamnatin jihar...

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...