Rikicin APC: Sanatocin APC Suna ganawa da Bola Tinubu

Date:

 

Ƴan Majalisar Dattijai na jam’iyar APC za su gana da jagoran Jami’yar na ƙasa, Bola Tinubu a yau Laraba da ƙarfe 2:30 na rana.

Shugaban Majalisar Dattijai, Ahmad Lawan ne ya baiyana haka a wata wasiƙa da ya karanta a farkon zaman majalisar na yau.

Jagoran majalisar, Sanata Yahaya Abdullahi (Kebbi ta Arewa), shi ne ya sanya hannu a wasiƙar.

“Akwai ganawa da jagoran Jami’yar APC, Snata Bola Ahmed Tinubu a yau 16 ga watan Maris 2022, in ji Lawan.

Za a yi ganawar ne a ɗakin taro na shugaban majalisar.

Duk da cewa ba a san batutuwan da za a tattauna a ganawar ba, wakilin mu ya jiyo cewa ba ta rasa nasaba da rikon shugabanci da ya dabaibaye APC.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Dan Majalisar tarayya daga Kano ya fice daga jam’iyyar NNPP

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Kano Municipal, Injiniya Sagir...

Abin mamaki: Barawo ya sace Motar dake cikin ayarin motocin gidan gwamnatin Kano

Wani barawon mota ya kutsa cikin gidan gwamnatin jihar...

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...