Daga Sayyadi Abubakar Gwagwarwa
Babban Sakataren Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Muhammad Abba Dambatta, ya karbi bakuncin tawagar hukumar NAHCON karkashin jagorancin Alhaji Usman Aliyu Shamaki, Daraktan duba aiyuka da bin ka’ida a yau Alhamis a Kano.
Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da jami’ar hulda da Jama’a ta Hukumar Jin dadin alhazai ta jihar kano Hadiza Abbas Sanusi ta sanyawa hannu kuma aka aikowa Kadaura24.
Tawagar ta zo Kano ne domin duba dukkan kayayyakin da ake bukata domin gudanar da aikin hajjin bana cikin nasara kuma sun ji dadin yadda shugaban tawagar ya mika godiyarsa ga Sakataren zartarwar hukumar bisa kyakkyawar tarba da aka yi musu.
A nasa bangaren, sakataren zartarwar Hukumar Abba Muhd Danbatta ya godewa tawagar bisa wannan ziyara tare da yin alkawarin ci gaba da shirye-shiryen da zasu sanya a samu cigaban aikin Hajjin bana.
Idan za’a iya tunawa Kadaura24 ta rawaito a farkon makon nan a wani taron manema labarai Sakataren zartarwar hukumar Muhd Abba Danbatta ya bayyana cewa hukumar ta Shirya caf domin tunkarar aikin Hajjin bana.