Ukraine ta buƙaci ‘yan Najeriya da ke son zuwa taya ƙasar yaƙi su biya dala 1,000

Date:

Mahukuntan kasar Senegal da kungiyoyin farar hula a Najeriya, sun yi alla-wadai da kiran da gwamnatin Ukraine ta yi wa ‘yan kasashen yammacin Afrika da su taimaka ma ta a yakin da take yi da Rasha.

Bayanai sun nuna cewa an samu mutane da dama da suka amsa kiran na jami’an gwamnatin Ukraine a wasu kasashen Afrika, domin yaki da Rasha.

Ma’aikatar harkokin wajen Senegal, ta ce sakon da ofishin jakadancin Ukraine ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya bukaci ‘yan kasar su tallafawa kasarsa a yakin da ta ke yi da Rasha.

Ofishin a sakon ya nemi duk wanda ya ke da aniyar taimakawar ya bada sunan shi da lambar waya da adireshin email.

Tuni dai aka samu kuma mutum 36 ‘yan Senegal da suka sanya hannu a kan takardar nuna aniyar taimakon Ukraine din.

BBC Hausa ta Rahotanni sun bayyana cewa an samu wasu ‘yan Najeriya da suka kai kan su ofishin jakadancin Ukraine da ke babban birnin kasar Abuja, tare da jaddada mubaya’a ga kasar domin yakar sojojin Rasha.

Sai dai jami’an ofishin sun shaida musu cewa kowanne zai biya dala 1,000 na sayan tikitin jirgi da bisar balaguron.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...