Gobara ta kone Rumbun adana kaya na Hukumar bada agajin gaggawa ta jihar kano

Date:

Daga Abdulrasheed B Imam
Wata gobara da ta tashi da yammacin ranar Juma’a a rumbun adana kaya na Hukumar bada  agajin gaggawa na jihar Kano (SEMA), Inda ta lalata kadarori na Naira miliyan 18.5 a mariri dake karamar hukumar Kumbotso.
 Sakataren zartarwa na SEMA, Dr Saleh Jili, ya tabbatar da hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a Kano ranar Juma’a.
 Ya ce lamarin ya afku ne a ranar Juma’a da misalin karfe 1 na rana a rumbun ajiya na SEMA dake Mariri inda rumbun yake cike makil da kayayyakin agaji da ake baiwa Waɗanda suka hadu da iftila’in gobara da ambaliyar .
 Yace gobarar ta tashi ne sanadiyyar kone yayi da akai a Makarantar first Lady, da ke kusa da rumbun, Inda azuzuwan dalibai uku suka kone kurmus sakamakon kona dajin wanda ya kara tsawaita wutar da ta kone wajen.
 Kayayyakin da gobarar ta lalata sun hada da katifu 450, matashin kai 450, katan 655 na Pampers na manya da yara.
 Sauran kayayyakin da suka kone sun hada da katon din Dettol guda 10, katan 10 na Sinadarin wanke-wanke, kwali 10 na Izal, injin nika, injin dinki, injinan fachi da gidan sauro, da dai sauransu, Waɗanda kudinsu ya kai Naira miliyan 18.5.
 Dr jili kuma yi kira ga jama’a da hukumomin makarantu da su Rika yi taka tsantsan wajen kona daji.
 Jili ya shawarci mazauna garin da su kasance dasu rika kashe kayan wutar lantarki a lokacin da za su fita daga gidajensu ko kuma kafin su kwanta barci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...