Ku fara shirin Hajjin 2022,NAHCON ta fadawa hukumomin alhazai na jihohi

Date:

 

Hukumar Hajji ta Ƙasa, NAHCON, ta umarci hukumomin alhazai na jihohi da su yi maza-maza su fara shirye-shiryen Hajjin 2022.

Shugaban Hukumar Hajji ta Ƙasa, Zikrullah Kunle Hassan, shi ya bada umarnin a Abuja a yayin ganawa da shugabannin hukumomin alhazai na jihohi a faɗin ƙasar nan.

Wannan matakin na NAHCON ya zo ne bayan da Hukumar ta samu umarnin hakan da ga Saudi Arebiya a kan fara shirye-shiryen Hajjin bana.

Hassan ya yi bayani cewa a bana, Hukumar Hajji da Ummara ta Saudiya ce za ta yi tsare-tsare da shirye-shirye na Hajji, ba kamar shekarun baya ba da hukumomin alhazai na ƙasashen waje ke shiga a yi shirye-shirye na kafin Hajji.

Shugaban NAHCON ɗin ya kuma umarci hukumomin alhazai na jihohi da su mayar da kuɗaɗen da alhazai su ka fara biya zuwa asusun adadin gata na Hajji da ke bankin jaiz domin a daidaita shirin na Hajjin 2022.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...