Cristiano Ronaldo zai koma PSG

Date:

Dan wasan gaban kungiyar kwallon kafa ta Manchester United Cristiano Ronaldo ya shirya komawa Paris Saint-German a karshen kakar nan.

Ronaldo dai yana samun kira daga PSG, Saboda suna shirya tsarin sallamar mai horas da Kungiyar Pochetteno su maye gurbin sa da tsohon kociyan Real Madrid Zinidine Zidane.

A cewar gidan jaridar El Chiringuito, Zidane wanda zai iya kasancewa kociyan PSG, Yana son yayi aiki tare da Cristiano Ronaldo a kungiyar.

Bayan Zidane ya karbi tabbacin cewar Neymar Jr da Lionel Messi zasu cigaba da zama a kungiyar hakan yasa yake son hadasu da Cristiano Ronaldo suyi wasa tare.

Ronaldo dai yana fuskantar matsi a Manchester United, Inda ake ganin idan har kungiyar ta gaza samun gurbin fafatawa agasar zakarun nahiyar turai shekara mai zuwa to babu makawa zai raba gari dasu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...