Gobara ta kone ofishin Rigakafi na karamar Hukumar Rogo kurmus

Date:

Rukayya Abdullahi Maida
A ranar Lahadin da ta gabata ne gobara ta kone ofishin rigakafi na kasa (NPI) dake karamar hukumar Rogo kurmos
 A jawabinsa a lokacin da yake karbar wata tawaga mai karfi daga hukumar kula da lafiya a matakin farko shugaban karamar hukumar Rogo Alh Mubarak Bashir Fulatan wanda mataimakins shugaban karamar hukumar Alhaji Sabiu Surajo Rogo ya wakilta ya bayyana cewa gobara har yanzu ba a san musabbabin tashin ta ba, ta lalata
Wuraren adana alluran rigakafi, Muhimman takardu da kuma ginin baki.
 Ya kuma bayyana cewa, karamar hukumar a nata bangaren ta ba da umarnin sashin aiyuka na karamar Hukumar domin tattara rahoton barnar da gobarar ta yi, domin baiwa karamar hukumar damar daukar matakan da suka dace.
Cikin Wata sanarwa da Jami’in hulda da Jama’a na Ma’aikatar Lafiya Matakin farko ta Jihar Kano Maikudi Muhd marafa ya aikowa Kadaura24, yace Tun da farko a nasa jawabin, babban sakataren hukumar kula da lafiya matakin farko ta jiha Dr. Tijjani Hussain wanda ya samu wakilcin Manajan shirin SERICC Dr. Habib Tijjani Gwarzo ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici Matuka.
Ya kuma bayyana Cewa gobarar ta kawo koma baya ga ayyukan rigakafi na yau da kullun a yankin.
 Dr. Tijjani ba ba da tabbacin cewa, za a dauki dukkan matakan da suka dace don samar da matakan gaggawa bayan tattara rahoton da Kwamitin ya tantance.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...