Abacha ya yaudari ‘yan siyasa – IBB

Date:

 

Tsohon shugaban mulkin sojin Najeriya Sani Abacha, wanda ya mulki kasar daga 1993 har lokacin mutuwarsa a 1998, ya hau mulkin ne bayan ya yaudari ‘yan siyasa, a cewar Janar Ibrahim Badamasi Babangida.

Janar Babangida ya bayyana haka ne a hirarsa da Trust TV, yayin da yake bayyana yadda Abacha ya yi yaudari mutane ya kwace mulki.

Abacha, wanda IBB ya bayyana a matsayin “babban abokina”, ya kasance hafsan hafsoshin sojoji a lokacin mulkin Babangida daga 1985, kuma daga baya ya nada shi Ministan Tsaro a 1990.

Babangida ya ce, gwamnatin Abacha tana da wayo. Sun san wadanda suka fi magana a kan zabe da juyin mulkin da batun 12 ga watan Yuni da sauran abubuwa.

Sai suka fara magana da su, suka yaudare su da karfafa musu guiwa su kawar da gwamnatin rikon-kwarya, da cewar idan sun kawar da gwamnatin rikon-kwaryar, za su dawo da su, su ba su abin da suke so mulkin dumokuradiyya, daga nan sai a kafa gwamnatin farar hula.

Babangida ya ce: ”Da wannan suka yaudari jama’a da sauran fitattun mutane, saboda haka da Abacha ya shigo, sai ake ta murna, hankali ya kwanta; Madalla abu ya yi kyau! Abin da zai faru a gaba kuma shi ne zababbiyar gwamnatin dumokuradiyya. Ni na sani, mun sani, hakan ba zai yiwu ba saboda maganar ita ce: (Abacha zai ce ), Me zai sa in sa kaina cikin hadari, kawai in zo in danka muku mulki?’ Wannan shi ne abin da ya faru.” In ji Babangida.

6 COMMENTS

  1. Assalamualaikum barka da rana Ina Yi muku fatan alkairi
    Duk haka kuke ba Amma gwanda irin su abachi da irin wadanan da suke mulki Naga mulkin sa yayi kokari Sosai duk da dai bani da wayo sosai

  2. I don’t know whether it’s just me or if perhaps everyone else experiencing issues with your site.
    It looks like some of the written text on your content are running off the screen. Can somebody else please
    comment and let me know if this is happening to them as well?
    This could be a issue with my web browser
    because I’ve had this happen previously.
    Thanks

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Kwamitin PTA na Kano ya dauki matakan hana ragewa dalibai hanya bayan taso su daga makaranta

DAGA ABDULHAMID ISAH Shugaban Kwamitin Iyayen yara da Malamai na...

Fada daba: Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Zuwa Ga Gwamnan Kano Alh. Abba Kabir Yusuf – Daga Zainab Nasir Ahmad

Daga Zainab Nasir Ahmad Mai Girma Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf Abba...

RATTAWU ta Kano ta taya Abbas Ibrahim Murnar sabon mukamin da NUJ ta ba shi

Kungiyar ma'aikatan Radio da Talabijin ta kasa reshen jihar...

NUJ ta kasa ta baiwa Abbas Ibrahim sabon mukami

Daga Aliyu Abdullahi Danbala   Kungiyar yan Jarida ta Nigeria ta...