Ban Yarda Namiji ba Dan Goyo Bane ba, Dan Goyo ne Kuma Har da Majanyi – Rukayya G/Kaya Ta Fadawa Mata

Date:

Daga Aisha Abubakar Mai Agogo

 

Shugabar Kungiyar “Sudu baba fulfulde” Kungiyar dake wayar da Kan Mata Kan harkokin Zaman Aure Hajiya Rukayya Gadon Kaya ta bukaci Mata Musamman Matan Aure su Rika daukar Mazajen su da muhimmanci yadda ya dace .

 

Kadaura24 ta rawaito Hajiya Rukayya Gadon Kaya ta bayyana hakan ne yayin wani taron wayar da Kan Mata, Wanda ya gudana a garin Dutse babban birnin jihar Jigawa.

 

Hajiya Rukayya Wacce ta ke ‘yar Jarida ce dake aiki a Gidan Radio Express dake Jihar kano, ta ce ya zama wajibi Mata su rika kula da hakkokin mazajesu Kamar yadda addinin Musulci.

 

Ni nayi Imani da duk duniya mijina shi ne maganin dukkan damuwata, Ina Kiran mata da suyi Imani da hakan Kuma Ina kira gare su, su rika girmama mazajensu Dan Allah ya shiga lamarinsu”. Inji Rukayya

 

Ta ce Allah ne ya ce mata su bi mazajesu Kuma tunda Allah ya fada babu shakka akwai Sakamakon da Allah zai baiwa duk wacce tabi mijinta, Wacce Kuma taki babu shakka zata sha azabar Allah.

 

Shugabar Kungiyar ta sudu baba fulfulde tace mace wayayyiya ita ce wacce ta ke bin mijinta sau da kafa Kuma ta ke yin duk Wani abun da zai faranta Masa ta ke Kuma barin duk abun da baya so.

 

Karya ne dai da ake cewa Namiji ba dan goyo bane, haka ban yarda da cewa duk wacce ta dau Namiji uba zata mutu Marainiya ba, waɗannan karin magana ne da akayi su tun lokacin jahiliya ba na duniyar ilimi ba” Rukayya ta jaddada

 

Taron dai ya Sami halartar Mata Masu tarin yawa , Waɗanda ake fatan taron wayar da Kan Masu Zai taimaka wajen dinke barakar da take tsakanin Masu fama da rikici tsakanin su day mazajen su , Waɗanda ko suke zaune lafiya da mazajensu zata Kara zaunar da su Lafiya.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...