Hadirin Mota a Kano yayi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 19, Mutane 26 Kuma Suka Sami Raunuka

Date:

 

Haɗarin mota ya yi sanadiyar rasuwar mutum 19, inda 26 kuma su ka ji raunuka a wani haɗarin mota a Bagauda, kusa da Makarantar Horas da Lauyoyi a kan titin Kano-Zariya.

Babban Kwamandan Hukumar kare Haɗarurruka, FRSC, a Jihar Kano, Zubairu Mato ne ya baiyana hakan a wata sanarwa da a ka raba wa manema labarai a yau Alhamis.

Ya ce motoci biyu haɗarin ya rutsa da su, waɗanda su ke ɗauke da lambobi kamar haka, KBT 152 XA da kuma NSR 275 ZX.

Mato ya ce rundunar ta samu kiran gaggawa ne da misalin 7:30 na a yau 6 ga watan Janairu, inda ya ƙara da cewa “Mu na samun rahoton, sai mu ka yi maza-maza mu ka tura jami’an mu da motoci, inda mu ka isa wajen haɗarin da misalin ƙarfe 7: 40 ma safe domin ceton fasinjojin.”

Ya yi bayanin cewa haɗarin ya afku ne sakamakon gudun wuce-sa’a da kuma ganganci, abinda ya haifar da karo goshi da goshi, inda duka motoci biyun su ka kama da wuta.

Ya ce mutane 45 ne a cikin motoci biyun, daga cikin su, 14 maza magidanta, mata magidanta 4 sai kuma karamin yaro namiji duk sun rasa rayukansu, inda 26 kuma su ka ji raunuka.

Ya ƙara da cewa wadanda su ka ji raunuka ai kai su asibitin Kura a na kulawa da su, yayin da gawawwakin waɗanda su ka rasu, an mika su ga iyalan su a caji-ofis na Bebeji.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...