Gwamnatin Tarayya ta Kara Harajin Naira 10 a Duk Kwalbar Lemo

Date:

Gwamnatin Najeriya ta ƙara harajin naira 10 kan duk wata lita da duka lemukan kwalba da ba giya ba, da sauran wasu lkayayyakin kwalama.

Wannan sabuwar dokar ma dauke ne cikin dokar kudi ta gwamnati ta 2021.

A cewar dokar an sanya wannan haraji ne domin rage yawan shan sikari wanda yake janyo ciwon siga da kuma kiba, da dai wasu abubuwan na daban.

Ministar kudi ta Najeriya Zainab Shamsuna Ahmed ta ce an samar da wannan karin kudin ne kan abubuwan da ke janyo rashin lafiya da kashe kudade ba bisa dalili ba.

Cikin kayayyakin da abubuwan suka shafa akwai Coca-Cola, Pepsi, Sprite da sauran abubuwan da suke janyo kiba saboda zakin da suke da shi.

BBC Hausa ta rawaito Rahotanni sun ce akwai kimanin ;’yan Najeriya miliyan hudu da ke fama da ciwon siga wanda ke da alaka kai tsaye da yawan shan siga da suke yi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Yusuf ya taya Dangambo murnar zama shugaban kungiyar mawallafa labarai ta internet na Kano

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir...

Hajjin bana: Za mu yi duk abun da ya dace don kyautata walwalar alhazan Jihar Kebbi – Amirul Hajji

Daga Ibrahim Sidi Muhammad Jega.   Shugaban kwamitin aikin hajin bana...

Bayan dawo da Gwadabe Anti daba, Yansanda sun kama yan daba 33 a Kano

Daga Rahama Umar Kwaru   Rundunar Yansanda ta Kasa reshen jihar...

Sabon Rikici ya Barke a Jam’iyyar NNPP ta Karamar Hukumar Dawakin Tofa

Rikici ya barke a cikin jam’iyyar NNPP ta karamar...