Gwamnatin Kano ta Kafa Kwamitin da Zai tabbatar Yan Kasuwar Kantin Kwari Sun bi Dokokin da akai Musu

Date:

Rukayya Abdullahi Maida

 

Gwamnatin jihar Kano ta kaddamar kwamitin karta-kwana domin bibiya tare da aiwatar da dokar hukumar gudanawar hukumar kula da kasuwar kantin kwari wacce majalisar dokokin jihar Kano ta yi.

 

Kadaura24 ta rawaito Da yake kaddamar da kwamitin, kwamishinan Kasuwanci cinika da masana’antu na jihar Kano Ibrahim Muktar ya ce an kaddamar da kwamitin ne domin kiyaye doka da gwamnatin jihar Kano ta yin a samar da hukumar kasuwar kantin kwari.

 

Ya ce anyi dokar karbar haraji da kuma aiwatar da wasu ayyuka da ma jagorancin kasuwar da nufin bunkasa harkokin kasuwanci.

Barista Ibrahim Mukar ya ce doka ce wani mutum ko wata kungiya ta rika karbar haraji a guraren yan kasuwa tare Kuma da rika bayyana wasu hanyoyi da za a bi wajen kasha kudaden.

Kwamishinan ya kuma bukaci yan kasuwa da su bawa kwamitin hadin kai domin samun nasara.

A jawabinsa Shugaban kwamitin kuma shugaban kasauwar kantin kwari Abba Muhammad Bello ya bada tabbacin za suyi duk mai yuwuwa domin sauke nauyin da ya rataya a wuyan su.

Abba Muhammad Bello yace Gwamnatin Jihar Kano ta yi dokokin Dan musgunawa yan Kasuwar ba,sai don a tsaftace harkokin Kasuwanci da Kuma Kara Dora Kasuwar akan tsarin doka da oga da kuma tafiya dai-dai da Zamani.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba ya yi Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wasu matasan Kano biyu a Benue

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi...

Rashin Jami’ar Mallakin jihar a shiyyar Kano ta Arewa na kokarin bayar da yankin baya – Alh. Mustapha Ahmad Gwadabe

Daga Shehu Hussaini Ahmad Getso An bukaci Gwamnatin jihar Kano...

Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Almuharram a Nigeria

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Fadar mai alfarma Sarkin Musulmi Alhaji...

Yan uwan wata mata sun zargi Asibitin Malam Aminu Kano da sakaci wajen mutuwar yar uwarsu

Daga Sadiya Muhammad Sabo   Yan uwan wata mata da ta...