Yan Sanda Sun Kashe Yan Bindiga 38 a Jihar Katsina

Date:

An kashe akalla ‘yan bindiga 38 yayin da ‘yan sanda biyar suka mutu a samame daban-daban da aka kai cikin jihar Katsina.

Rundunar ‘yan sanda jihar Katsina ce ta bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da ya gudana karkashin shugaban ‘yan sandan jihar Sanusi Buba.

Babu shakka wannan shekarar da ta kare an fuskanci kalubale mai yawa a Katsina musamman na tsaro, sai dai rundunar ‘yan sandan jihar ta samu nasarori masu yawa a yakin da take da ‘yan bindiga da masu satar mutane da ‘yan fashi da sauran manyan laifuka da ake aikatawa.

Duk da haka 2021 cikinta an samu raguwar wadannan laifuka idan aka kwatanta da 2020″.

Cikin rikicin an samu nasarar kashe ‘yan bindiga 38 an kuma kashe mana jami’ai 5.”

Rundunar ta ce an kama wasu da ake zargi da muggan ayyuka 999 da suke da alaka da manyan laifuka 608.

A gefe daya kuma an kama wasu mutum 874 na daban da aka gurfanar gaban shari’a a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...