GAP ta yabawa Ganduje bisa nadin Lamin a matsayin mai ba shi shawara kan harkokin kananan hukumomi

Date:

Daga Abubakar Sa’eed Sulaiman
 Wata Kungiyar mai suna Grassroot Administration Platform (GAP) mai hedkwata a Arewacin Najeriya, ta yabawa gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje bisa nada Lamin Sani Zawiya a matsayin mai ba shi shawara kan harkokin kananan hukumomi da masarautu.
 Da suke yaba wa nadin a Cikin wata wasika da suka aike wa gwamnan mai dauke da sa hannun Shugaban kungiyar, David Samuel Gidanwaya, sun ce irin wannan nadin ya dace duba da kwarewar wanda aka nadan.
 Wasikar ta ce, “A matsayinsa na tsohon Shugaban kungiyar Shugabanin Kananan Hukumomi ta Jihar Kano (ALGON) tun daga Shekarar 2018 zuwa 2021 kuma tsohon Shugaban Karamar Hukumar Nassarawa, nadin nasa ya nuna irin jajircewar Gwamnan wajen samar da ingantaccen tsari Gudanar da kananan hukumomi.”
 “Nadin Lamin Sani da Mai Girma Gwamna ya yi, wata alama ce da ke nuna cewa jihar Kano ta ba da muhimmanci sosai wajen ci gaban al’umma tun daga tushe,” a cewar wasikar.
 A sanarwar da Babban Sakataren yada labaran Gwamnan Malam Abba Anwar ya aikowa Kadaura24 yace kungiyar ta GAP Sun kuma bayyana cewa, tun a zamanin da Lamin Sani yake shugaban karamar hukumar Nassarawa suke bi sahun sa Kuma sun gamsu da irin cigaban da ya kai yankin.
 “Daga cikin shawarar da muka yanke, mun yi imanin Sabon Mai ba da shawar taimakawa wajen ciyar da kananan hukumomi yadda ya kamata zuwa mataki na gaba.”

2 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...