Zargin ta da hargitsi: Tsagin Ganduje sun yi Karar Tsagin Shekarau wajen IG

Date:

Daga Rukayya Abdullahi Maida

Bangaren Gwamnan Jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje sun zargi tsagin Sanata Malam Ibrahim Shekarau da kokarin tada tarzoma a jihar kano ,ta hanyar sayan Makamai da Kuma tunzura Matasa.
Hakan na kunshe ne cikin takardar korafin da Suka rubutawa Babban Sufeton Yan Sanda na Kasa wadda Sanata Kabiru Gaya da Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar wakilai Hon. Alhassan Ado Doguwa da wasu yan Majalisun jiha dana Tarayya guda da Shugabanin Kananan Hukumomi suka Sanyawa Hannu.
A Cikin takardar sun bukaci Babban Sufeton Yan Sandan da ya Gudanar da bicike tare da daukar Matakin gaggawa akansu don Samar da Zaman Lafiya a Jihar Kano.
Cikin takardar korafin da Kadaura24 ta samu ta nuna yadda aka yi sitamfi na Ofishin Babban Sufeton Wanda hakan ke nuna Ofishin ya karbi takardar korafin ta su.
Idan ba’a mantaba Kadaura24 ta rawaito a kwanakin bayan tsagin Sanata Malam Ibrahim Shekarau Suma sun rubuta makamancin irin Wannan takarda ta korafi ,Inda Suka zargi tsagin Gwamna Ganduje da Kona ofishin Sanata Barau Jibril a Ranar 30 ga Watan Nuwanba 2021.

1 COMMENT

  1. קמגרה תשדרג לכם את חיי המין ותאפשר לכם הנאה מרבית מהאקט. לטבע פלז’ר שלל פתרונות טבעיים נוספים שישדרגו לכם את חדר המיטות. קמגרה תשדרג לכם את חיי המין ותאפשר לכם הנאה מרבית מהאקט. לטבע פלז’ר שלל פתרונות טבעיים נוספים שישדרגו לכם את חדר המיטות. מכוני ליווי

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...