Fati Muhammad ta sake dawowa Kanywood, bayan Shekaru 14 da barin masana’antar

Date:

Daga Maryam Adamu Mustapha

 

Fitacciyar jarumar fina-finan Hausa Fati Muhammad ta dawo Kannywood bayan shafe shekaru goma sha hudu da daina sana’ar.

Dawowar Fati ta kasance tare da fatan alheri daga masoyanta da masoyan fina-finan Hausa.

Ta dawo ne a matsayin mai shirya fina-finai kamar yadda wata ‘yar gajeriyar sanarwa ta bayyana a shafin Facebook na ‘Kannywoodcelebrities.

A Ranar talatar nan dai sabbin hotunan Jarumar sun karade shafukan Sada Zumunta musamman Facebook da instegram Wanda hakan ke nuni da Cewa al’umma Suna farin Ciki da dawowarta harkar Fina-finan Hausa.

KADAI ta rawaito an dai nuna hoton Fati Muhd a zaune kan Wata kujera yayin da ake daukar wani sabon fim Wanda zata taka rawa a Cikin sa, Kuma za a iya Cewa Shirin shi ne na Farko bayan dawowarta harkar Fina-finan Hausa.

Fati ‘yar asalin jihar Adamawa ta fara harkar fim tun tana karama, Fina-finan ta da suka yi fice a Cikin su sun hada da Sangaya, Zarge, Marainiya, Mujadala, Kudiri, Tutar So, Garwashi, Tawakkali, Gasa, Abadan Da’iman, Zo mu Zauna, Tangarda, Hujja, Al’ajabi, Halacci, Samodara, Zumunci, Murmushin Alkawari, Gimbiya, Bakandamiya, Taskar Rayuwa, Babban Gari da dai Sauransu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gidauniyar Aliko Dangote za ta rabawa ‘yan Najeriya miliyan daya shinkafa

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Gidauniyar Aliko Dangote ta raba buhunan...

Rufe Makarantu da azumi: Ministan Ilimi ba ta da ilimin harkokin mulki – Jafar Sani Bello

Daga Aliyu Danbala Gwarzo   Tsohon dan takarar gwamnan jihar Kano...

Da dumi-dumi Dangote ya sake rage farashin man fetur a Nigeria

Daga Rahama Umar Kwaru   Matatar mai ta Dangote ta bayyana...

Akwai bukatar kebe rana ta musamman a matsayin ranar tsofaffin dalibai a Kano – Kwamared Waiya

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim...