Yan sanda a Kano sun Gano Gawar Mace da Namiji a Mota

Date:

Yan sanda a Kano sun ce sun gano gawar mutane biyu a kurar bayan wata motar kirar Siena a kan hanyar zuwa Katsina.
 Kano Fucus ta rawaito rahotonnin sun nuna cewa binciken ya gano sunan mutumin da ya mutu a Matsayin Steven Ayika yayin da macen aka bayyana sunan ta a Matsayin Chiamaka Emmanuel dukkanin su mazauna unguwar Jaba ne dake nan Kano.
 A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar a ranar Alhamis, ya ce: “A ranar 23/11/2021 da misalin karfe 0450 na safe, an samu rahoton cewa an ga wata mota a kan hanyar Katsina, dake karamar hukumar Fagge ta jihar Kano dauke da mutane biyu (2) a ciki, namiji daya Mace daya.
 “Bayan samun rahoton, kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, CP Sama’ila Shu’aibu Dikko, fsi, ya taso tare da umurci tawagar ‘yan sanda da su wuce wurin da lamarin ya faru.
 “Nan take tawagar ta garzaya wurin da lamarin ya faru.  An kwashe gawawwakin, inda aka garzaya da su Asibitin kwararru na Murtala Mohammed Kano, yayin wani Likitan lafiya ya tabbatar da mutuwarsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...