Shugaban Karamar Hukumar Kumbotso ya lashi takobin Kawo Karshen Matsalar tsaro

Date:

Daga Zainab Muhd Darmanawa
Karamar hukumar Kumbotso ta kaddamar da wasu jami’an kula da tsaro guda 100 da suka hadar da ‘yan sintiri da mafarauta  a yunkurin ta na inganta tsaron yankin.
Kadaura24 ta rawaito Shugaban karamar hukumar, Alhaji Garban Kauye Farawa ne ya sanar da hakan, yayin gudanar  da wani taron masu ruwa da tsaki akan al’amuran tsaro a yankin, yana mai karawa da cewa kowanne daga cikin jami’an zai rika karbar kudaden alawus na Naira dubu 20 kowanne wata.
Farawa ya kuma kara da cewa karamar hukumar zata ginawa jami’an ofishi na din-din-din, a daidai lokacin ya mikawa  ofishin ‘yan sanda na unguwar Ja’o’ji sabuwar motar sintiri kirar Sharon Domin inganta tsaro a yankin.
Hakazalika farawa ya Raba sababbon mashi nan hawa guda 10, inda ya  baiwa jami’an Sintiti na Vigilante Sabon babur 5, kirar CIB 1, kwamandan Hisba Kuma an bashi 1, DSS 1, mafarauta 1, sai Kuma jami’an yan sanda da Suma suka Rabauta da guda 2 Domin fadada Harkar Sintirinsu da tsaro a Karamar Hukumar.
Cikin wata sanarwa dauke dasa hannun Mai Taimakamasa Kan harkokin yada labarai Shazali farawa ya Rawaito cewa, a nasa bangaren mai martaba sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, wanda ya samu wakilcin Hakimin Kumbotso, Alhaji Ahmad Ado Bayero ya bada tabbacin cewa dukkannin masu rike da sarautun gargajiya a yankin, zasu bada gudunmawar data dace wajen kare lafiya da dukiyoyin al’umma, tare da yabawa Shugaban karamar Hukumar bisa wannan namijin kokari.

2 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano za ta sake gina Masallacin da aka kona a Gezawa

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna...

Hukumar shari’a ta Kano ta ladaftar da wasu ma’aikatan kotu

Daga Usman Hamza   Hukumar Kula da Harkokin shari'a ta Jihar...

2027: Malam Shekarau ya bayyana matsayar kungiyarsu kan hadakar yan hamayya a Nigeria

Ƙungiyar siyasa ta Northern Democrats, ƙarƙashin jagorancin Malam Ibrahim...

Da Ɗumi-Ɗumi: Dangote ya sake rage farashin man fetur

Matatar man fetur ta Dangote ta sanar da ƙarin...