Sheikh Gumi ya Gina Makaranta a Daji don Makiyaya a Kaduna

Date:

Daga Abdulmajid Habib Isa Tukuntawa
Fitaccen malamin addinin Musuluncin nan, Ahmad Gumi, ya gina makarantar makiyaya a Kagarko da ke kusa da dajin kauyen Kohoto a matsayin hanyar magance matsalar rashin tsaro a jihar Kaduna.
 Kamar yadda Jaridar Daily Trust ta ruwaito, malamin ya sanyawa makarantar sunan cibiyar Sheikh Uthman Bin Fodio.
 Gidauniyar Sultan Mosque Foundation Limited ce ta dauki nauyin gudanar da aikin don Ilimantar da makiyayan Saboda su guji Shiga harkokin ta’addanci.
 “Idan sun yi ilimi, ba za su yi abin da suke yi ba” inji Gumi
 “Saboda haka, muka ce Bari mu Fara Samar musu da ilimi tun daga tushe, kuma mun fara aikin don ya zama abin koyi ga kananan hukumomi, jihohi da tarayya da kuma masu hannu da shuni da  kungiyoyin hadin gwiwa da su Zo mu hada Kai mu tabbatar an Ilimantar da makiyayan don duk abin da suke Rashin ilimi ne yake haddasa su.
Kadaura24 ta rawaito da ma dai Shehun Malamin ya Dade Yana fadin Rashin ilimi ne yake haddasa ta’addancin da makiyayan keyi, Kuma ya bada tabbacin idan Suka Sami Ilimi za su dai na abubuwan da suke.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamna Abba Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Gaya Polytechnic

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sanya...

Sojoji sun mikawa Tinubu Shawarwari yadda za a kawo karshen matsalar tsaron Nigeria

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya karɓi rahoton dakarun sojan...

Shugaba Tinubu ya sake nada Buba Marwa a matsayin shugaban NDLEA

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake tabbatar da nadin...

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Koma Jam’iyyar APC a Hukumance

Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar...