Magance talauci: Shugaban Kano Poly yana ba da tallafin Naira dubu 100 ga al’ummar D/Tofa kowanne wata

Date:

Daga Musa Mudi Dawakin Tofa
Mazabar Kwa dake yankin Karamar hukumar Dawakin Tofa ita ce mazaba ta hudu cikin mazabu goma sha daya da al’ummarta suka amfana da tallafin Shugaban Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta jihar Kano Dokta Kabir Bello Dungurawa a ranar Lahada 7/11/2021.
A yayin taron bada tallafin Dr Kabiru Dungurawa ya ce suna zabo mutane ashirin marayu da marasa karfi maza da mata ne don basu tallafin, kuma mazabar Kwa ita ce mazaba ta huda ta amafana a wannan rana cikin mazabun dake karamar hukumar Dawakin tofa.
Dr Kabir Bello Dungurawa ya kara da cewa la’akari da halin matsin rayuwa da al’ummar karkara ke ciki yasa Gwamna Kano ya basu dama ta shugabanci, saboda haka a duk karshen wata “nake cire naira dubu dari daga albashinna don tallafawa mabukata ashirin a kowacce mazaba dake karamar hukumarta”.
“Ina fatan wannan ɗan tallafi zai taimakawa wadanda suke amfana da tallafin wajen inganta rayuwar da ta makusantansu”. inji Dr Dungurawa
Kungiya Malamai makarantun gaba da sakandire ‘Yan asalin karamar hukumar Dawakin Tofa su aka dorawa alhakin zakulowa tare da tantance duk waɗanda za su amfana da tallafin.
 Wakilin Shugaban Kungiyar malaman wanda kuma shi ne Ma’ajin Kungiyar Malam mai suna malam Junaidu Dalladi ya ce sun zabo marayu, nakassu da masu karamin karfi don basu tallafin, ya kuma yi kira ga duk wadanda suka amfana da tallafin kudin  da su yi amfani dasu ta hanyar da ta dace.
Malam Junaidu Dalladi ya kuma yi kira ga duk masu hali da suya koyi da tallafin dan Kungiyarsu wato Dokta Kabir Bello Dungurawa don ragewa al’umma raɗaɗin halin matsi da ake ciki.
Taron bada tallafin ya gudana a makarantar Firamare dake garin Kwa yankin karamar hukumar Dawakin Tofa a masarautar Bichi.
Al’ummar garin kwa musamman waɗanda suka ci gajiyar tallafin sun godewa Dr Kabiru Dungurawa bisa wannan tallafi ,tare da bada tabbacin zasu yi amfani da tallafin ta hanyar da ta dace.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An sanya dokar hana fita a Jigawa

An sanya dokar hana fita a Jihar Jigawa tare...

Gwamnan Kano ya bayyana abun da gwamnatin za ta yi a filin Idi

  Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sanar...

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...