Garban Kauye ya nuna alhininsa Kan hadarin Daliban Sa’adatu Rimi

Date:

Daga Nura Abubakar

 

Shugaban karamar hukumar Kumbotso Hon Hassan Garban kauye farawa ya Bayyana Damuwa gami da kaduwa da samu labarin Rasuwar Daliban kusan 5, Yan makarantar kwalajin ilimi ta sa’adatu Rimi, sakamakon Hadarin mota akan haryar Kano zuwa katsina.

Cikin Wata sanarwa da Mataimaki na mis Kan harkokin yada labarai ga Shugaban Karamar Hukumar Shazali Saleh farawa ya aikowa Kadaura24 yace Shugaban karamar hukumar ta Kumbotso Cikin Alhini ya Aike da sakon Ta’aziyya ga Mai Girma Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje, kwamishiniyar ilimi Mai zurfi Dr mariya Bunkure da shugaban Kwalajin Dr yahaya Isa Bunkure da Kuma Daliban makarantar, sai iyayen Daliban Yan Uwa da abokan arziki sai Kuma Al’ummar jihar Kano musamman na karamar hukumar Kumbotso.

Cikin wani sako Ta’aziyya Daya wallafa Dauke dasa Hannun maitaimaka Masa na musamman Kan harkokin yada labarai Shazali Farawa, alhaji Hassan yace.

“Innalillahi wa inna illaihir Raji’un, Ina Adu’ar Allah ya jikansu, yakai Rahama kabarinsu ya Kuma baiwa marasa lafiyan cikinsu koshin lafiya”

Akarshe yace Allah Daya karbesu yafimu son su, Yana Kuma Amfani da wannan Dama wajen Mika sakon Ta’aziyyar ga kungoyoyin Dalibai bisa wannan Baban Rashi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Rundunar yansanda ta kasa ta aiko sabon kwamishina Kano

    Hukuamr Ƴansanda ta Najeriya ta amince da naɗi CP...

Yadda akai na bukaci Tinubu ya sauya sunan FCE Kano zuwa sunan Maitama sule

Daga Rahama Umar Kwaru   Mataimakin shugaban majalisar dattawan Nigeria Sanata...

Shugabannin hukumar zakka ta Kano sun ziyarci Sarki Sanusi II

Daga Sani Idris maiwaya   An bukaci Hukumar Zakka da Hubusi...

Nimet ta bayyana jihohin da za su fuskanci tsananin zafi

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargaɗin...