Ƴan sanda sun ceto mutum 47 daga wani gidan mari a Kano

Date:

Ƴan sanda sun ceto mutum 47 daga wani gidan mari a jihar Kano.

Gidan da ake bayyanawa da gidan gyaran hali wuri ne da iyaye kan tura ‘ya’yansu da ke muggan dabi’u da shaye-shaye da aikata manyan laifuka.

Lokacin da ‘yan sanda suka kai samame a ranar Alhamis, sun ceto mutum 47 duk maza da shekarunsu ke tsakanin 14 zuwa 35 sanye da sarkoki. Jikinsu duk dauke ya ke da alamar duka.

Kakakin ‘yan sanda Abdullahi Haruna ya shaidawa BBC cewa an cafke mutumin da ke da gidan mari kuma za a gabatar da shi a kotu.

Gwamnatin jihar dai ta haramta irin wadannan gidaje watanni 10 da suka gabata bayan kai sameme a ire-iren wadannan gidaje da ake cin zarafi ko azabtar da mutane da sunan tarbiyya.

‘Yan uwa da iyayen yara na cewa su na aike yaransu irin wadannan wurare ne saboda rashin cibiyoyin gwamnatin na gyara hali.

Mutanen da ake ceto yanzu haka na samun kulawa a asibiti.

2 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta dakatar da Dadin kowa, Labarina, Jamilun jidda da wasu fina-finai 19

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   A kokarinta na tabbatar da ana...

2027: Hon Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana Matsayarsa kan takarar gwamnan Kano

Daga Zakariya Adam Jigirya   Dan Majalisar tarayya mai wakiltar kananan...

Sarkin Yaƙin Garko, ya ɗauki nauyin dubawa da raba magunguna kyauta ga marasa lafiyar 1400 a Garko

  Sarkin Yaƙin Garko, mai kishin al'umma, kuma ɗan jam'iyyar...

NAHCON ta yi jigilar Maniyatan Nigeria Sama da 24,000 zuwa Saudiyya a kwanaki 10

Daga Khadija Abdullahi Aliyu   Hukumar Kula da aikin hajji ta...