Gwamnatin tarayya ta umarci kamfanonin wutar lantarki da su kara kudi wata daga 1 ga Satumba.

Date:

Daga Nasiba Rabi’u Yusuf

Hukumar da ke kula da lantarkin Najeriya ta amince da sake duba karin farashin wutar lantarki a kasar nan.

An sanar da hukuncin hukumar ne a cikin wata takarda ga kamfanonin rarraba wutar lantarki.

Kadaura24 ta rawaito Gwamnatin tarayya ta hannun Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Najeriya (NERC) ta umarci Kamfanonin Rarraba Wutar Lantarki (DisCos) dake kasar nan da su kara farashin harajin su daga ranar 1 ga Satumba, 2021.

Jaridar Guardian ta ruwaito cewa an tabbatar da ƙarin a cikin takarda daga Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Eko, mai kwanan wata 25 ga Agusta, 2021, mai lamba 023/EKEDP/GMCLR/0025/2021.

Takardar ta bayyana cewa Karin zai karu daga N42.44 zuwa 58.94 ya danganta da ajin su.

Ana sa ran sabon karin aikin zai ci gaba da aiki har zuwa watan Disamba kafin a kara samun karuwa a watan Janairun 2022.

Kungiyar Kwadago ta Najeriya wacce ke kalubalantar Kudirin na karin kudin wutar lantarki har yanzu ba ta mayar da martani ga sabon hukuncin da Gwamnatin ta dauka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Shugabannin Hukumomi a Kano Sun Yaba Da Ayyukan Abba, Sun Nemi Ya Nemi Wa’adi Na Biyu

Kungiyar shugabannin hukumomi da ma'aikatun gwamnatin jihar Kano ta...

Idan mu ka rungumi Addu’o’i ba abun da Amurka za ta iya yiwa Nigeria – SKY

Shahararren ɗan kasuwa a Kano, Alhaji Kabiru Sani Kwangila...

Shugaban APC na Kano Abdullahi Abbas ya Magantu Kan Zargin raba Ramat da Kujerarsa

Shugaban jam’iyyar APC na Jihar Kano, Alhaji Abdullahi Abbas,...

Iftila’i: An tsinci gawar wata dattijuwa mai shekaru 96 cikin rami masai a Kano

A ranar Alhamis al’ummar ƙauyen Sarai da ke ƙaramar...