Duniyar Aikin Jarida ta yi rashin Isa Abba Adamu tsahon Shugaban BBC Hausa

Date:

Daga Zainab Muhd Darmanawa

Allah ya yiwa kwararen Dan Jaridar nan Kuma tsohon Ma’aika’cin Sashin Hausa na BBC Isa Abba Adamu Rasuwa.

Isa Abba Adamu ya rasu ne a Lahadin nan a birnin London na Kasar Birtaniya.

Cikin Wata sanarwa da Dan uwan Mamacin yusha’u Adamu Wanda ya yi aiki Gidan Jaridar Daily Trust yace za a binne Isa Abba Adamu a can birnin Landan, Amma yace “duk da haka, akwai Salatil Gha’ib a gidan danginmu tare dake Lamido Crescent kusa da Express Radio da ƙarfe 9 na safe. Muna bukatar addu’o’in ku”. Inji Yusha’u

Marigayi Isa ya taba zama shugaban Sashin BBC Hausa a shekarar 1990 sannan kuma ya rike Babban Editan na BBC Afrika.

Wasu daga cikin abokan aikin Isa Abba Adamu sun bayyana Mamacin Matsayin Mutum Mai girmamawa da kiyaye lokaci. “Yana cikin gidan Bush kullum da ƙarfe 6 na safe yake gudanar da tarurrukan lokacin da yake shugaban Afirka da Gabas ta Tsakiya Kuma yayi shubanci abin koyi.” Allah ya jikansa da rahama Amin.

Kadaura24 ta rawaito cewa Bashir Gentile gudane cikin Waɗanda Suka mu’amalanci Mamacin ya Kuma bayyana shi a Matsayin Mutum na gari da a koda yaushe yake kula da aikinsa. Ya Kuma ce Rashin sa ba karamin Rashi bane mai girma ga Duniyar Aikin Jarida.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano za ta sake gina Masallacin da aka kona a Gezawa

Daga Maryam Muhammad Ibrahim   Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna...

Hukumar shari’a ta Kano ta ladaftar da wasu ma’aikatan kotu

Daga Usman Hamza   Hukumar Kula da Harkokin shari'a ta Jihar...

2027: Malam Shekarau ya bayyana matsayar kungiyarsu kan hadakar yan hamayya a Nigeria

Ƙungiyar siyasa ta Northern Democrats, ƙarƙashin jagorancin Malam Ibrahim...

Da Ɗumi-Ɗumi: Dangote ya sake rage farashin man fetur

Matatar man fetur ta Dangote ta sanar da ƙarin...