Tsawa ta Kashe Mutane 16 yayin da suke Daukar Hoto

Date:

Tsawa ta kashe a ƙalla mutum 16 tare da jikkata wasu da dama a garin Jaipur da ke arewacin Indiya a ranar Lahadi.

Mutanen suna ɗaukar hoton “selfie” ne a cikin ruwan da ake sheƙawa a saman wata hasumiya da ke wani gini mai tarihi na yawon buɗe ido.

Mutum 27 ne ke kan ginin da kuma bangon a lokacin da abin ya faru, kuma rahotanni sun ce wasu daga cikin su sun yi tsalle sun faɗa ƙasa.

A ƙalla mutum 2,000 tsawa ke kashewa duk shekara a Indiya.

Wani babban jami’in ɗan sanda ya shaida wa kafafen yaɗa labarai cewa mafi yawan mutanen da suka rasun matasa ne.

A ranar Lahadi kaɗai an samu rahotannin mutuwar mutum tara a faɗin jihar Rajasthan inda Jaipur yake, a cewar kafofin yada labaran yankin.

Rahotanni sun ce ana kuma samun rahotannin mutuwa a sauran jihohi sakamakon faɗuwar tsawa.

An ruwaito cewa a ƙalla mutum 41 – mafi yawa mata da yara ne tsawa ta kashe a gundmomin jihar Uttar Pradesh. Mafi yawan waɗanda suka rasun mutum 14 a birnin Prayagraj suke.

Manyan ministocin Uttar Pradesh da Rajasthan sun sanar da biyan dala 6,700 a matsayin diyya ga iyalan waɗanda suka rasun.

Ofishin Firaminista Narendra Modi ma ya sanar da biyan dala 2,681 ga iyalan mamatan a dukkan jihohin uku.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Tinubu ya taya tsohon Gwamnan Kano, Shekarau murnar cika shekaru 70

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon Gwamnan...

Abdulmumin Kofa ya koma APC tare da bayyana goyon bayansa ga Tinubu

Abdulmumin Jibri Kofa, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Kiru...

Labari mai dadi: Nahcon ta rage kudin kujerar hajjin 2026

Shugaban hukumar NAHCON Kula da aikin hajji ta Nigeria ...