Harin Yan Bindiga: Shugaban Kasar Niger ya jajantawa Ganduje

Date:

Daga Abubakar Sa’eed Suleman

Shugaban Kasar jamhoriyar Niger Muhd Bazoum ya jajantawa gwamnati da al’ummar jihar Kano bisa ga iftila’in hari da yan bindiga Suka kaiwa tawagar gwamnan kano a Lokaci da suke Kan hanyar su ta dawowa daga jihar Zamfara

Muhd Bazoum ya bayyana hakan ne lokaci da ya jagoranci Wata tawaga zuwa Gidan gwamnatin jihar Kano domin yiwa Gwamna Ganduje jaje.

Shugaban Kasar Wanda Gwamnan jihar Damagaran dake jamhoriyar Niger Alhaji Musa Isa ya Wakilta yace abun da ya faru abun takai ci me.

Yace matsalar Tsaro da ta addabi kasashen Nigeria Camaro da Niger jarrabawa ce Daga Allah Kuma yayi fatan Waɗanda Suka Jikkata Allah ya basu lafiya ya kiyaye hakan a nan gaba.

Bazoum yace sun zo Kano ne domin taya Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero Murnar bashi Sanda da aka yi a Ranar Asabar din data gabata.

Yace sun yaba sosai da irin Karramawar da aka yi musu kafin taron lokacin taron da bayan taron,Amma yace basu yi mamakin karramawar ba idan akai la’akari da dangantakar dake tsakanin Kano da Niger.

A nasa jawabin Gwamnan kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya yabawa ayari bisa amsa gayyatar da aka yi musu ,Sannan yayi musu fatan kokawa gidan lafiya.

77 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Iftila’i: An sanya dokar hana fita a Jigawa

An sanya dokar hana fita a Jihar Jigawa tare...

Gwamnan Kano ya bayyana abun da gwamnatin za ta yi a filin Idi

  Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sanar...

Ba zaben 2027 ne a gaba na ba – Tinubu

    Fadar shugaban Najeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu...

Rikicin Masarauta: Gwamnatin Kano ta Bayyana Matsayarta Kan Hukuncin Kotu

Daga Rukayya Abdullahi Maida   Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano kuma...