Nada Sarkin Kano Aminu zai zama silar hade kan Arewa-Abdulaziz Yari

Date:

Daga Nusaiba Sani Darma

Tsohon Gwamnan jihar Zamfara Alhaji Abdulaziz Yari Abubakar ya bayyana nada Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero a Matsayin Sarkin Kano da cewa hanyace ta dinke Arewacin Nigeria.

Alh. Abdulaziz Yari ya bayyana hakan ne Yayin da yake ganawa da Manema labaran gidan gwamnatin jihar Kano.

Abdulaziz Yari yace sarkin Kano mutum ne da yake son cigaban al’ummar yankin Arewa Kuma yake Kaunar Zaman lafiya a Koda yaushe.

“Na zo kano ne domin taya Dan uwana Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero Murnar Bikin bashi Sanda da za’a yi Ranar Asabar a Matsayin Sarkin Kano na 15 a Sarakunan fulani” inji Yari

” Ina taya al’ummar jihar Kano dana Arewacin Kasar nan Murnar Wannan Lokaci Kuma Ina fatan za’a yi bukukuwan Cikin kwanciyar hankali da lumana .”Inji shi

Kadaura24 ta rawaito Yari ya Kuma yi fatan al’ummar Kano Zasu cigaba da baiwa Sarkin hadin Kai domin ya Sami damar yiwa al’umma adalci da Kawo Cigaba.

105 COMMENTS

  1. Усик – Джошуа: появились промо JoshuaUsyk Бій Усик – Джошуа за звання чемпіона світу за версією WBA, WBO та IBF відбудеться в Лондоні. Місцем його проведення стане стадіон футбольного клубу “Тоттенгем”. Щодо дати проведення бою, то

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Subscribe

Mafi Shahara

Karin Wasu Labaran
Related

Gwamnatin Kano ta yi karin haske kan batun goyo a babur

Gwamnatin jihar Kano ta ce masu sana’ar Achaba Kawai...

Kwamishinan shari’a na Kano ya gana da kwamishinan ’Yansanda kan korafe-korafen kama masu goyo a babur

Babban Lauyan Gwamnatin Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru...

Mai ciki ta mutu bayan ma’aikacin asibiti ya ƙi yarda a biya kuɗi ta waya

Wata mata mai ciki, Aisha Najamu, ta mutu a...

Kungiyoyin Arewa sun gargadi Tinubu kan shigo da Yakubu Dogara cikin Gwamnatinsa

Wasu kungiyoyin matasa da na zamantakewa-siyasa daga Arewa maso...